Rahotanni da suka bayyana yanzu nan an ji Cewar wutar lantarki ya fara dawowa a jihohi hudu da ke karkashin hukumar Rarraba Wutar Lantarki ta Jos wadannan jihohi su ne Filato, Bauchi, Gombe, da kuma Benue.
KU KARANTA : Nan Da Kwanaki Biyar A Tsammaci Wutan Lantarki – Minista Ya Magantu
Wutar dai ta dawo ne da misalin karfe 7:20 na daren yau laraba. Wakilin Daily Trust ya ruwaito cewa mazauna garin Jos, babban birnin jihar Filato sun fito cikin murna da jin dadi.
In ba a manta ba WikkiTimes ta ruwaito cewa, a cikin kwanaki 10 da suka gabata, an sami matsalar daukewar wuta a wasu jihohin arewacin kasar nan.



