Manoma daga garuruwa 23 sun gudu sun bar muhallansu bayan ‘yan bindiga sun karbe iko da sansanin horon soji mafi girma na Nigeria da ke jihar Niger.
Rahotanni sun bayyana cewa sansanin horon sojojin, wanda ya mamaye wani yanki na karamar hukumar Kontagora da karamar hukumar Mairiga, ya koma karkashin ikon ‘yan ta’adda dauke da manyan bindigu.
Akwai fargabar cewa barin garuruwansu da manoman su ka yi zai iya haifar da karancin abinci a Nigeria.
Labarin wannan abin takaici ya fito ne daga bakin mamba a majalisar dokoki ta jihar Niger yayin da ya gabatar da batun a zauren majalisar domin su tattauna halin da sansanin horon sojoji na Nagwamase a karamar hukumar Kontagora ya ke ciki.
A cewar mambobin majalisar, kwace iko da sansanin sojin ya sake haifar da sabuwar barazanar tsaro ga jami’an rundunar soji da sauran jama’a da ke zaune yankin.
KARANTA: Zamfara: Sojoji sun kashe Jagororin ‘Yan Bindiga Biyu; ‘Black’ Da Kachalla
KADUNA: Jama’a Sun Kone Gawarwakin ‘Yan Bindiga a Kachia
Nigeria Za Ta Ci Bashin $16m Domin Siyo Jiragen Yaki 6 Daga Kasar Italy
Abdullahi Isah, mamba mai wakiltar mazabar Kontagora II, shine wanda ya gabatar da kudirin neman majalisar ta gaggauta daukan mataki a kan lamarin.
Ya kara da cewa zaman ‘yan bindiga a sansanin sojojin ya kara yawan adadin hare-haren da ake kai wa garuruwan da su ke makwabta da sansanin, lamarin da ya tilasta jama’a guduwa daga gidajen su domin neman mafaka.
Majalisar ta nuna damuwa a kan yadda ‘yan bindigar su ka mayar da muhimmin wurin bawa sojoji horo na Nagwamase sansanin su. Sansanin ya kasance wuri na musamman domin bawa sojoji horo kafin tura su wuraren da za su yi aiki a fadin Nigeria.
‘Yan majalisar sun yi kira ga gwamnatin jihar Niger a kan ta gaggauta daukan mataki domin ganin an fatattaki ‘yan bindigar domin zaman lafiyar mazauna yankin har ma da jami’an tsaro.



