Kotun Majistare a Jos ta Yanke wa Makiyayi Hukuncin Wata Tara a Kurkuku Saboda Dukan Wata Mace
A ranar Alhamis, wata kotun Majistare a Jos ta yanke wa wani makiyayi mai shekaru 41 mai suna Isa Mohammed hukuncin wata tara a gidan yari saboda dukan wata mace.
Alkalin Kotun Majistare Shawomi Bokkos ne ya yi shari’ar ta gaggawa kuma ya yanke masa hukunci bayan ya amsa laifin da aka tuhume shi da shi.
KARANTA WANNAN: Bauchi: Kotu Ta Yankewa Mutumin Da Ya Yiwa Yarinya Fyaɗe A Masallaci Ɗaurin Rai Da Rai
Kotu Ta Kori Kakakin Majalisar Dokokin Filato
Kotu Ta Ba Da Belin Likitan Da Ke Saida Sassan Jiki A Jos
Bokkos, wanda ya yanke masa hukuncin wata tara a gidan yari, ya ba shi zabin biyan tarar N50,000 tare da biyan diyyar N30,000 ga mai shigar da kara.
Tun da farko, mai gabatar da kara, Insifeta Ibrahim Gokwat, ya shaida wa kotu cewa an kai karar ne a ranar 27 ga watan Agusta, a ofishin ‘yan sanda na “C” Division da ke Jos, daga Hassana Sambo, wacce ita ce mai shigar da kara.
Gokwat ya ce wanda ake tuhuma ya doki matar sannan ya lalata wayarta wadda kudin ta ya kai N45,000.
Ya ce laifin ya saba wa kudin laifuka da hukunce hukuncen su na jihar Filato. (NAN)



