spot_imgspot_img

Bauchi Da Wasu Jihohin Arewa 7 Da Har Yanzu Babu Labarin Karin Albashi

Jihohi goma sha bakwai ne a fadin Nigeria da har yanzu babu wani labari dangane da shirin da suke yi na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N70,000 da aka amince da shi, lamarin da ya jefa ma’aika a wadannan jihohi cikin fargabar rashin sanin lokacin da zasu fara cin moriyar karin.

Daga cikin wadannan jihohi guda goma sha bakwai, akwai takwas daga cikinsu da suka fito daga yankin arewa wadanda har yanzu babu wata niyya da suka nuna domin karawa ma’aikatan su albashi.

WikkiTimes ta yi tankade tare da rairaya wajen zakulo wadannan jihohi na arewa da suka hada da Bauchi, Kwara, Nasarawa, Plateau, Sokoto, Taraba, Yobe, da Zamfara. Hakazalika, gwamnatin babban birnin tarayya (FCT), Abuja, ba ta bayyana matsayar ta ba.

KARANTA: Yadda Wani Kauye Ya Noma Shinkafa Don Gina Sabon Ajin Makaranta A Bauchi

Bauchi : SUBEB Ta Gayyaci Malamai 57 AKan Fashin Zuwa Aiki

Bayan Barazana Ga Mawallafin WikkiTimes, Dan Gwamnan Bauchi Ya Yi Barazanar Maka Dan Bello A Kotu

Gwamnan Bauchi Ya Yiwa Sarakuna Kyautar Nunawa Sa’a

Har yanzu jihohi kalilan ne suka yi wani hobbasa wajen ganin sun kaddamar da sabon karin albashi daga N30,000 zuwa N70,000 da shugaban kasa, Bola Tinubu, ya yi bayan an kai ruwa rana tsakanin gwamnatinsa da kungiyar kwadago (NLC).

Rahoton WikkiTimes ya bayyana cewa ya zuwa yanzu jihohi 18 ne a cikin 36 suka fara biya ko kuma suka yi alkawarin fara biyan sabon mafi karancin albashi na N70,000 ga ma’aikatansu.

Sauran jihohin Nigeria da har yanzu ba a ji duriyar su dangane da shirin da suke na fara biyan sabon albashin ba sun hada da Ekiti, Edo, Delta, Bayelsa, Akwa Ibom, Imo, Cross River, da Enugu.

Naziru Taura
Naziru Taurahttp://wikkitimes.com/hausa
Naziru Taura is a dedicated teacher, Hausa blogger, freelancer, and translator with a passion for education, information dissemination, and purposeful leadership. He specializes in crafting compelling stories in both English and Hausa, focusing on the Sustainable Development Goals (SDGs) and amplifying the voices of marginalized and underreported communities. Through his work, Naziru offers hope, advocates for justice, and drives meaningful conversations on societal progress. With over a decade of experience, Naziru has produced numerous impactful stories, shedding light on business and economic empowerment opportunities. His investigative work has also uncovered cases of corruption, abuse of power, and the mismanagement of public funds, showcasing his commitment to accountability and transparency.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Most Read

Latest stories