Gwamnatin jihar Yobe ta fara mayar da mutanen da ambaliyar ruwan sama ta lalatawa gidaje zuwa sabon matsugunin da aka samar mu su.
Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, shine da kan sa ya kaddamar da fara yin hijirar mutanen Kirikasamma da ke yankin karamar hukumar Geidam.
Sakataren hukumar bayar da agajin gaggawa a jihar Yobe (SEMA), Muhammad Goje, shine ya sanar da hakan a shafin sa na dandalin sada zumunta, Facebook, yayin da ya ke jaddada manufar gwamnati na kawo karshen matsalar ambaliyar ruwan sama da mazauna yankin ke fuskatanta.
“Tsawon shekaru kenan da mutanen garin Kirikasamma fiye da 500 su ke zaman wucin gadi a garin Geidam bayan ambaliyar ruwan sama ta yi sanadiyyar rushewar gidajen su 114. Yawancinsu su na zaune ne a rukunin gidajen Mai Mala,” a cewar sa.
A cewar Muhammad, gwamnati ta gudanar da bincike mai zurfi, wanda ya hada har da na tsaro, kafin fara rabawa wadanda abin ya shafa sabbin matsuguni da zasu zauna tare da iyalansu domin sake gina sabuwar rayuwa.
KARANTA:Â YOBE: ‘Yan Sanda Sun Kama Wata Mata Mai Shekaru 54 Da Alburusai 350
Jigawa Za Ta Ci Moriyar Shirin Bunkasa Noma Da Bankin Duniya Ya Ware $500m
Ƴan Sanda Sun Cafke Wani Magidanci Bisa Zargin Kisan Matarsa a Yobe
Fitinannen Mai Garkuwa Da Mutane Ya Fada Komar ‘Yan Sanda A Yobe
Ya bayyana cewa an fara shirin mayar da su sabon matsugunin a hukumance ta hanyar fara raba mu su kudi da kayan amfani wanda hukumar SEMA ta jagoranta.
Ya kara da cewa gwamnatin jiha ta ware fili mai girman hekta 8.53 a matsayin muhalli da wurin noma ga kowanne Magidanci tare da bayyana cewa an basu wuraren ne kyauta da sharadin mutum ba zai bayar ga wani ba.
Muhammadu ya ce ana cigaba da samar da sauran kayan more rayuwa da suka hada da ruwa mai tsafa, makaranta, da asibiti domin moriyar mutanen.
Babban sakataren ya tabbatar da cewa an samu hadin kai da goyon bayan ma su ruwa da tsaki da suka hada da karamar hukumar Geidam, Ma su rike da sarautar gargajiya, wakilan sarkin Ngazargamu, da jami’an tsaro kafin fara sauyawa mutanen matsuguni.



