Rundunar ‘yan sanda a birnin Dutse, jihar Jigawa, ta tabbatar da konewar wasu gidaje hudu kurmus a yayin da wata mata da yaran ta suka tsira da kyar bayan wani direba da ake zargin a buge ya ke ya kutsa kai da mota cikin wani gida.
A cewar rundunar ‘yan sandan, lamarin ya faru ne a daren ranar Lahadi yayin da wata mota, da ake zargin direban ta ya kwankwadi barasa kafin ya hau tuki, ta ture katangar wani gida da wata mata da yaran ta su ke ciki su na bacci.
Shiisu Lawal Adam, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa, shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin, wanda ya ce ya yi sanadiyyar rushewar gidan tare da tashin gobarar da ta shafi karin wasu makwabtan gidaje guda uku.
A cewar sa, da kyar jama’ar unguwa da hadin gwuiwar jami’an tsaro su ka samu nasarar shawo kan gobarar. Ya kara da cewa binciken farko da su ka fara gudanarwa ya gano cewa direban motar ba a cikin hayyacinsa ya ke ba.
KARANTA:Â JIGAWA: FG Ta Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa A Dutse A Kan Biliyan N59.4
Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe N117m Domin Samar Da Cibiyar CNG A Dutse
Jigawa: An gano Ma’aikatan Bogi 6,348 Da AKe Kashewa 3.7bn A Matsayin Albashi
“A Sakamakon hakan, da motar da gidan duk sun kone kurmus, sannan kuma lamarin ya shafi sauran wasu makwabtan gidaje guda uku, wadanda su ma su ka kone kurmus,” a cewar Shiisu.
Ya kara da cewa duk da ba a samu asarar rai ba, an samu nasarar ceton matar tare da yaran ta, amma an samu asarar dukiya ta miliyoyin Naira.
“Duk da cewa, ba a samu asarar rai ba. Binciken da mu ka fara gudanarwa ya gano cewa mai motar sunan sa Muhammad Galadima wanda shi ne da gangan ya bawa Abdullahi Abubakar Sadiq makulin motar, wanda shi kuma ya tabbatar mana da cewa bai iya tuki ba”, kamar yadda Shiisu ya bayyana.



