Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da sakin kudi, biliyan N1.5, domin fara biyan bashin hakkokin ma’aikatan jihar da su ka yi ritaya.
Kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’ada, Sagir Musa, shi ne ya sanar da hakan ta cikin wani jawabi da ya fitar ranar Talata a garin Dutse.
Sagir ya bayyana cewa majalisar zartarwa ta jiha ta amince da sakin kudin ne yayin zaman ta a ranar Talata.
Ya kara da cewa sakin kudin wata alama ce da ke kara nuni a kan manufar gwamnatin Jigawa a karkashin jagorancin gwamnan jihar, Umar Namadi Danmodi, na inganta walwalar ma’aikatan da su ka yi ritaya tare da biyan su hakkokin su a kan lokaci.
JIGAWA: FG Ta Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa A Dutse A Kan Biliyan N59.4
Jigawa: An gano Ma’aikatan Bogi 6,348 Da AKe Kashewa 3.7bn A Matsayin Albashi
Kwamishinan ya ce za a saki kudin zuwa hukumar kula harkokin fansho wacce a karshe za ta tura kudin zuwa asusun tsofin ma’aikatan da su ke bin gwamnati bashin hakkin sallama kamar yadda ofishin shugaban ma’aikatan jiha ya tantance ya kuma gabatar yayin zaman su na ranar Talata.
A cewar sa, Gwamnan jihar Jigawa ya jaddada kudirin sa na inganta walwala da nutsuwar ma’aikata, hatta a lokacin da su ka yi ritaya. (NAN).



