spot_imgspot_img

Borno: Mayakan Boko Haram Sun Kashe Manoma Fiye Da 40 A Sabon Hari

Wasu ‘yan ta’adda da ake kyautata zaton cewa mayakan kungiyar Boko Haram ne sun kashe manoma fiye da 40 a wani sabon hari da su ka kai kauyen Kayakura a yankin karamar Kukawa a jihar Borno.

Lamarin, wanda ya yi sanadin raunata wasu manoman ma su yawa, ya faru ne da misalin karfe 4:30 na yammacin ranar Lahadi.

Mazauna yankin sun shaidawa jaridar Daily Trust cewa mayakan sun kai harin ne a mazabar Doron Baga, inda su ka bude wuta a kan jama’a.

“Maganar da mu ke yi, yanzu haka ba a san inda mutane da yawa su ke ba, sannan sun kashe manoma fiye da 40 da su ka gujewa harin ‘yan kungiyar Boko Haram daga karamar hukumar Gwoza,” kamar yadda wata majiya ta shaidawa Daily Trust.

KARANTA: Borno: An Tsare Shugaban Jam’iyyar NNPP Saboda Sukar Gwamna Zulum

Dakarun MNJTF Sun Dakile Harin ISWAP A Jihar Borno

Gwamnatin Jihar Borno Ta Wanke Mutane 500 Da Ake Zargi Ƴan Boki Haram Ne

Sabon harin ya faru ne bayan kwana daya da kai wani hari a garin Chibok, kudancin jihar Borno, inda mayakan su ka kashe mutane biyu tare da kone wata Coci.

An samu mabanbantan rahotanni a kan adadin mutanen da su ka mutu. Wata majiyar jami’an tsaro ta sanar da cewa mutane 30 ne mayakan su ka hallaka.

“Mutane 30 sun rasa rayukan su sakamakon harin da aka kai wa Manoma a yankin Doron Baga,” kamar yadda majiyar jami’an tsaro ta sanar da Daily Trust.

Kokarin Daily Trust na jin ta bakin Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Borno, ASP Kenneth Daso, bai samu ba saboda wayar sa ba ta shiga a lokacin da aka kira shi.

Naziru Taura
Naziru Taurahttp://wikkitimes.com/hausa
Naziru Taura is a dedicated teacher, Hausa blogger, freelancer, and translator with a passion for education, information dissemination, and purposeful leadership. He specializes in crafting compelling stories in both English and Hausa, focusing on the Sustainable Development Goals (SDGs) and amplifying the voices of marginalized and underreported communities. Through his work, Naziru offers hope, advocates for justice, and drives meaningful conversations on societal progress. With over a decade of experience, Naziru has produced numerous impactful stories, shedding light on business and economic empowerment opportunities. His investigative work has also uncovered cases of corruption, abuse of power, and the mismanagement of public funds, showcasing his commitment to accountability and transparency.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Most Read

Latest stories