spot_imgspot_img

Gwamnatin Bauchi Ta Rufe Dukkan Makarantu Saboda Fargabar Tsaro

Gwamnatin Jihar Bauchi ta bada umarnin rufe dukkan makarantun firamare, sakandare da manyan makarantu a fadin jihar nan take, sakamakon karuwar matsalolin tsaro.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Jalaludeen Usman, Jami’in hulda da jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Bauchi, ya fitar, inda aka bayyana cewa dokar ta shafi dukkan nau’ikan makarantu na gwamnati, na tarayya da kuma na masu zaman kansu.

Sanarwar ta bayyana cewa an dauki wannan mataki ne bayan shawarwari masu zurfi da kuma nazari kan barazanar tsaro da ke yi wa dalibai, malamai da al’ummomin makarantu barazana.

Gwamnati ta ce duk da cewa matakin ba mai sauki ba ne, dole ne a dauke shi domin kare rayuwar yara, wanda ita ce babbar alhakin gwamnati.

Gwamnati ta roki iyaye, masu kula da yara da kuma masu makarantu su kwantar da hankula su kuma guji rudani, tana mai tabbatar da cewa hukumomin tsaro na aiki tare da ita don magance matsalolin cikin gaggawa tare da dawo da yanayi na karatu da zarar an tabbatar da tsaro.

Haka kuma an shawarci jama’a su kasance masu kula da tsaro a unguwanninsu, su rika bayar da rahoton duk wani abin da ya saba tsari, domin hakan na taimakawa wajen kare al’umma.

Gwamnatin jihar ta yi alkawarin ci gaba da sanar da jama’a duk wani sabon abu da ya taso kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Most Read

Latest stories