spot_imgspot_img

Atiku Abubakar Ya Karɓi Katin Zama Ɗan Jam’iyyar ADC

A wani muhimmin lamari da ya ja hankalin jama’a, tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya karɓi katin zama ɗan jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a mazaɓarsa da ke Jada, Jihar Adamawa.

Rahotanni sun nuna cewa Atiku ya karɓi katin ne bayan kammala shiri da tattaunawa da manyan jagororin jam’iyyar, lamarin da ke nuna sabuwar hanyar siyasar da yake shirin ɗauka a gaba.

Wannan mataki ya jawo ce-ce-ku-ce a fagen siyasa, inda ake kallonshi a matsayin sabon babi a harkokin jam’iyyun Najeriya da kuma shirya shiryen siyasar da ke gabatowa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Most Read

Latest stories