Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta sanar da gano tare da daƙile barazanar kai hari da wasu mutane suke shirin yi a sirrin ce a ranar sallah.
Kwamishinan ƴan sandan jihar, Muhammad Usaini Gumel, a wata ganawa da ya yi da malaman addinin musulunci da kuma wakilai daga masarautun Kano guda biyar a ranar Litinin din da ta gabata, ya ce ƴan sanda sun gano wasu mutane da ke gudanar da ayyukansu a cikin kungiyoyin musulmai domin tada tarzoma.
Kwamishina Gumel ya kara da cewa rundunar ƴan sanda da sauran hukumomin tsaro a jihar sun gaggauta kawo daƙile shirin kai harin da aka yi shirin yi dama wanda ake ƙoƙarin yi lokacin bukukuwan Sallah da kuma bayan sallah.
Ya bayyana mutanen da ke kokarin aikata ta’asar da ƙaryar cewa su ƴan Qadiriyya ne,duk da cewa shugaban darikar, Sheikh Qaribullah Kabara ya nesanta kansa da waɗannan mutane ta hanyar nuna goyon bayan zaman lafiya.