Sakataren Harkokin Wajen Amurka Blinken Ya Gana Da Shugaba Tinubu A Abuja

Sakataren harkokin wajen Amurka, Anthony Blinken ya isa Najeriya a wani bangare na rangadin mako daya zuwa kasashen yammacin Afirka hudu.

Amurka na fafutukar ganin dorewar tasirinta yayin da take samun gogayya daga ƙasashen Rasha da China.

Kasashe a yammacin Afirka musamman a yankin Sahel sun fuskanci karuwar matsaloli ciki har da sauye-sauyen gwamnatoci a hudu daga cikin mambobin kungiyar ECOWAS 15.

Ziyarar ta zo ne daidai lokacin da Abuja, babban birnin Najeriya ke fuskantar matsalolin tsaro da sace-sacen jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Most Read

Latest stories