A jiya Laraba ne majalisar dattawa ta amince da buƙatar shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu Na karɓo rancen dala miliyan 500 domin samar da mitocin wutar lantarki a kasar.
An aminta karɓar kuɗin ne ga Hukumar Kamfanonin Gwamnati (BPE) bayan an yi nazarin rahoton kwamitin majalisar dattijai mai kula da basukan gida da waje wanda mataimakin shugaban kwamitin, Sanata Haruna Manu (Taraba ta tsakiya) ya gabatar.
Rancen kuɗin na daga cikin lamunin dala biliyan 7.94 na bankin duniya wanda shugaba Bola Tinubu ya nemi amincewar majalisar dattawa tun a ranar 1 ga Nuwamba, 2023.