Bayan Wuya : Ɗan Najeriya Ya Zama Gwarzo A Boko,Ya Halarci Firamari 16

Jajircewa Da juriya ya sa Ɗan Najeriya Emmanuel Oluwasayomi Ahmadu ya sami lambar girmamawa biyu a ƙasar Amurka inda a halin yanzu yake karatun digirinsa.  

Labarin jajircewa da juriyar Emmanuel ta kasance wani bangaren da ya samo asali sakamakon juriya da hakuri.

Sanuwar Emanuel idon duniya ya samu asali ne a shekarar 2018 lokacin da ya lashe lambar yabo ta ƙasa da ƙasa na yammacin Afirka yayin da yake karatun digiri sa na farko a Jami’ar Benin (UNIBEN). 

Babban abin mamaki game da Emanuel shi ne irin yadda tun tasowar sa ya fuskanci ƙalubalen rayuwa wanda har haka ta sa ya yi tsalle-tsallen karatun firamare , Emanuel Sai da halarci makarantun firamare ɗai-dai har guda 16 makarantun sakandare 14 saboda halin rayuwa.

A cigaba da gwagwarmayar karatu sai da  Emmanuel ya shafe shekaru biyar yana zana jarrabawar O’level a lissafi ya yi zaman jarabawar sau 17 kenan .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Most Read

Latest stories