Tsohon Sanata mai wakiltar Kaduna ta tsaƙiya, Shehu Sani, ya danganta matsalar tsaro da tattalin arzikin da ke addabar yankin Arewa ga ƴan siyasar yankin.
Shehu Sani, wanda ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa da aka yi da shi da gidan talabijin na Channels a ranar Lahadi, ya ce ƴan siyasar yankin Arewa ba su yi amfani da karfin kujerun su ba wajen amfanar al’ummar su.
A cewarsa, duk al’amuran da ke faruwa a Arewa sun faU ne“sakamakon rashin samun ingantaccen shugabanci” a yankin.
- Jihohin Arewa 8 Da Ambaliyar Ruwan Kogi Zata Shafa A Watan Yuli – FG Ta Yi Gargadi
- KADUNA: ‘Yan Bindiga Sun Saki Babbar Alkaliya, Sun Rike ‘Ya’yanta Uku
- Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Yi Korar Ma’aikata
- NDLEA : Za A Fara Yiwa Ma’aurata Gwajin Ƙwaya A Kano
- Sanadiyyar Ƙwallo Wani Matashi Ya Rasa Ransa A Jami’ar Tarayya Da Ke Gombe
“Kun ga Ni ɗan Arewacin Najeriya ne ɗan Jihar Kaduna, kuma idan akwai wani wuri, da zan so in ga ci gaban sa da jama’a suna zaune lafiya, da samun damar gudanar da harkokinsu na yau da kullum,shi ne inda na fito. ” cewar Shehu Sani
Shehu Sani ya cigaba da cewa duk da irin ƙarfi da ƴan Arewa suka yi a siyasa amma duk da haka yankin na fama da matsalolin rashin tsaro, talauci, da yaran da ba sa zuwa makaranta .