A yau ne rahotanni suka bayyana cewar Ƴan bindiga sun sako sauran ɗaliban jami’ar Gusau da ke tsare a hannun su .
A zantawa da BBC ta yi da wata ƴar uwar ɗaya daga cikin waɗanda aka sace ta bayyana cewa a jiya Asabar ne suka sami kira daga ƴar uwar su cewa an yi nasarar karɓo su hannun ƴan bindigar daga dajin Birnin Gwari suna Abuja .
In ba a Manta ba a watannin baya ne dai ƴan bindiga su ka dira ɗakunan kwanan ɗalibai mata na jami’ar inda suka yi awon gaba da ɗalibai da dama.