Gwamnan jihar Kastina, Dikko Radda ya ce ƙoƙarin gwamnatinsa na ganin ta yi yaki da ƴan bindiga yana samun tazgaro sakamakon zagon ƙasa da wasu daga cikin mutane ke yi wajen haɗa kai da ƴan bindiga suka kai musu bayanai.
Gwamna Radda ya bayyana haka ne a lokacin da yake ganawa da manema labarai a ranar bikin cikarsa shekara ɗaya akan mulki.
Gwamnan ya ƙara da cewa yadda ƴan Bindiga ke samun bayanan sirri ko Gwamnati ba ta samu kamar haka.