Wasu ‘yan ta’adda da aka fi zaton ‘yan bindiga ne sun kai hari wani kauye a Jihar Sokoto inda suka kashe mutane da yawa tare da yin awon gaba da wasu da sa’o’in farko na safiyar ranar Asabar.
Maharan sun dira a kauyen Dudun Doki da ke yankin karmar hukumar Gwadabawa a Sokoto tare da kashe fiye da mutane goma da kuma wasu da dama.
Jaridar Vanguard ta rawaito cewa lamarin ya faru ne misalin karfe 1:30am na safiyar ranar Lahadi, ranar da Musulmi a fadin duniya ke murnar bikin babbar Sallah.
Akwai karin bayani…….