AFCON: Shugaba Tinubu Ya Roƙi Super Eagles Da Su Doke Kamaru A Wasan Gobe

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya roki ‘yan wasan Super Eagles da su yi duk mai yiwuwa don ganin sun samu nasara a yayin da Najeriya zasu fafata da babbar abokiyar hamayyarta, Kamaru a gobe, domin buga wasan dab da na kusa da na karshe a gasar cin kofin nahiyar Afirka da ake yi a Cote d’Ivoire. .

An isar da sakon shugaban kasar ga tawagar ta hannun ministan raya wasanni, Sanata John Owan Enoh, inda ya bukaci Super Eagles da su jajirce wajen tunkarar abokan karawarsu a wasan zagaye na 16 mai mahimmanci na gobe asabar.

Kamar yadda wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimakiya ta musamman ga sanata Enoh, Diana-Mary Tiku Nsan, ta bayyana cewa ‘yan Super Eagles sun sanar da cewa shugaban kasar na bin kungiyar ne domin yayi duk abinda ya dace a kansu, don haka dole ne su rubanya kokarinsu domin ‘yan Nijeriya da suke gida su samu Farin ciki da wannan wasa .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Most Read

Latest stories