Gwamnatin tarayya ta hoɓɓasa ta biya bashin dala miliyan 850 da kamfanonin jiragen sama na Turai ke binta kamar yadda kungiyar Tarayyar Turai EU ta bayyana.
Jakadiyar Tarayyar Turai a Najeriya da kungiyar ECOWAS, Samuela Isopi,ita ce ta bayyana hakan a wajen taron kasuwanci da ya gudana tsakanin Najeriya da EU karo na 9 a Abuja.
KU KARANTA :
- Yarjejeniyar Samoan: Gwamnatin Tarayya Zata Maka Daily Trust A Kotu
- Kotu Ta Umarci Sadiya Umar Farouq Ta Yi Bayanin Yadda Ta Raba N729bn Ga Talakawa Miliyan 24.3 Cikin Wata 6
- Mata Da Miji Masu Safarar Ƙwaya Sun Shiga Hannun NDLEA
- NYSC : Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙarawa Masu Yiwa Ƙasa Hidima Alawus
- An Sake Samun Matsalar Lalacewar Wutar Lantarki
Taron mai taken ‘Zuba hannun jari don amfanin gaba mai dorewa’ wanda ya samu halartar babban darakta a kungiyar ta EU, Myriam Ferran, ministan kasafin kuɗi da tsare-tsare na ƙasa, Atiku Bagudu, da kuma babban sakatare a ma’aikatar masana’antu, Ciniki, da Zuba Jari, Ambasada Nura Rimi.
A wajen taron, EU da Eurocham Nigeria (The European Business Chamber) sun rattaɓa hannu kan yarjejeniyar bayar da tallafi na Yuro 300,000 don tallafa wa ci gaban haɗakar.