A wata ziyarar gani da ido da Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya kai gidan maza dake ciki garin Kano domin ganin yadda shirin ciyarwa azumi ke gudana gwamnan ya nuna ɓaci ransa matuka.
![](https://wikkitimes.com/hausa/wp-content/uploads/2024/03/IMG_8856.jpeg)
A faifan bidiyo da ya bayyana an dai ga gwamnan ya tsare masu dafa abincin yana tuhumar su cikin ɓaci rai sakamakon ganin irin ƙasƙantaccen abincin da suke dafawa .
Gwamnan dai ya yi kakkausar jan kunne game da wannan lamari inda ya shaida cewa baya so ya sake dawowa ya ga an maimaita irin hakan.