Sai Kun Yi Haƙuri, Amma Sai Gwamnati Ta Ɗauki Matakai Masu Tsauri – Buhari

Tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Talata ya buƙaci ƴan Najeriya da su yi haƙuri da gwamnatin tarayya, yana mai cewa za a ɗauki wasu tsauraran matakai.

Buhari ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake gabatar da wani littafi mai suna ‘Aiki tare da Buhari,’ wanda tsohon mai ba shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Femi Adesina ya rubuta.

Taron ya samu halartar manyan baƙi da suka haɗa da magajinsa, Bola Tinubu da tsohon shugaban ƙasa da Janar Yakubu Gowon (rtd) da uwargidan shugaban ƙasa, Remi Tinubu da Aisha Buhari da tsohon mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo da Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio da wasu da dama.

A cikin jawabin nasa, Buhari ya nemi afuwar mutanen da suka gamu da ajalinsu na wasu zafafan matakai da gwamnatinsa ta ɗauka.

“Mun adana tarihin aikinmu da sanin cewa koyaushe za a buƙaci mu yi lissafin amanar da aka ba mu. Wannan littafin da muke ƙaddamarwa a yau na daga cikin lissafin wa’adin mulkin mu guda biyu, kuma na shaida wa waɗanda suka yi aiki dare da rana, da su tabbata an rubuta wannan tarihi domin yanzu da kuma nan gaba,” in ji shi a taron da aka yi a Abuja.

“Gwamnati ci gaba ce; kamar tseren yada ƙanin wani ne. Kuna yin naku, kuma sai ku miƙa sandar mulki ga mutum na gaba. Bola Ahmed Tinubu na yanzu yana da goyon bayana da kuma ƙwarin gwiwa a kan ƙokarinmu na ganin mun samu ƙasar da muke burin samu, inda za a sami ƴanci ga dimbin al’ummarmu.”

Ya kuma yabawa tsohon kakakin nasa Adesina bisa kokarin da aka yi wajen tattara nasarorin da gwamnatinsa ta samu a cikin littafin, inda ya ce kyakkyawan aikin ya zama hanyar yin hisabi a wurin ƴan Najeriya.

“Ba tare da takaddun shaida ba, yawancin mutane suna da ɗan gajeren tunani. Wasu mutane za su zo su yi ƙoƙari su karkata ko ma shafe tarihin kwanan nan. Amma abin lura a gare mu shi ne, ba a yi wani abu a cikin rufin asiri ba. Mu masu gaskiya ne da rikon amana kamar yadda zai yiwu kasancewar muna sane da gaskiyar cewa zuriya ita ce babban alƙali.”

Buhari ya mulki Najeriya a matsayin shugaban kasa daga 2015 zuwa 2023 ya kuma miƙa wa magajinsa, Tinubu bayan ya kammala wa’adinsa na biyu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Most Read

Latest stories