Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Operation Hadarin Daji (OPHD) sun yi nasarar daƙile wani yunkurin yin garkuwa da wasu mutane 10 da ƴan bindiga su ka yi ƙoƙarin yi a garin Tsafe da ke jihar Zamfara a jiya Talata.
A cewar jami’in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar Suleiman Omale, a wata sanarwa da ya fitar a Gusau a yau Laraba,ya ce sojojin ba su yi ƙasa a gwiwa ba suka yi nasarar daƙile harin.
“Mun sami kiran gaggawa a daren ranar 12 ga watan Maris, 2024 inda sojoji suka dira garin tare da farwa ƴan bindigan.
“Jajircewa, ya sa sojojin yin nasara akan ƴan bindigar inda suka gudu kowanne su da raunuka tare da barin waɗanda suka sace.